Isa ga babban shafi
Najeriya

Yawan mutanen suka mutu sakamakon rushewar dogon bene a Legas ya kai 38

Hukumomi a jihar Legas dake Najeriya sun ce adadin wadanda suka mutu sakamakon rugujewar wani bene mai hawa 21 a unguwar Ikoyi ya kai 38, a yayin da aka fara yanke kauna ga samun wadanda ke da sauran numfashi.

Gwamnan Jihar Legas baba Jide Sanwo-Olu yayin ganawa da wasu Iylai da 'yan uwan wadanda hatsarin rugujewar gini ya rutsa da su a unguwar Ikoyi. 4 ga watan Nuwamba, shekarar 2021.
Gwamnan Jihar Legas baba Jide Sanwo-Olu yayin ganawa da wasu Iylai da 'yan uwan wadanda hatsarin rugujewar gini ya rutsa da su a unguwar Ikoyi. 4 ga watan Nuwamba, shekarar 2021. © RFI Hausa / Michael Kuduson
Talla

Michael Kuduson da ya ziyarci wurin ya hada mana rahoto a kai.

01:30

Halin da ake ciki dangane da aikin ceto mutanen da gini mai hawa 21 ya rubzawa a Legas

A Alhamis din nan ne dai jami'an ceto dake kokarin ciro mutanen da suka makale a karakashin ginin  mai hawa 21 da ya rushe a Legas suka tabbatar da mutuwar Femi Osibona, shugaban Kamfanin Fourscore Homes Limited, wanda ya rasu sakamakon rutsawar da rubzawar ginin yayi da shi. Osibona dai shi ne mamallakin kamfanin da ya gina benen mai hawa 21 da ya ruguje a unguwar Ikoyi dake Legas a ranar Litinin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.