Isa ga babban shafi
Najeriya - Noma

Rikicin Boko Haram ya hana manoma fiye da dubu 65 zuwa gonakinsu - FAO

Hukumar Bunkasa Noma ta Majalisar Dinkin Duniya FAO, ta yi gargadi game da karancin abinci a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.

Wani manomi a yankin Arewa maso gabashin Najeriya.
Wani manomi a yankin Arewa maso gabashin Najeriya. © FAO
Talla

FAO ta ce matsalar Boko Haram ta hana manoma kimanin dubu 65 da 800 samun gudanar da ayyukan gona a yankin.

Wakilin FAO a Najeriya, Fred Kafeero ne ya bayyana haka yayin bikin kaddamar da ayyukan noman rani na wannan shekara a Maiduguri.

Rahoto kan halin da noma ke ciki a Arewa maso Gabashin Najeriyar na zuwa ne adaidai lokacin da mazauna karamar Hukumar Kala Balge a Jihar Barno ke kokawa kan yadda Giwaye suka addabi ayyukansu na noma, kamar yadda Kaumi Ali Ngalama ya shaidawa sashin Hausa na RFI.

Kaumi Ali Ngalama kan yadda Giwaye suka addabi manoma a wasu sassan jihar Borno
00:41

NIGERIA-2021-06-24-KAUMI

Yankin Arewa maso Gabashin Najeriya dai na daga cikin yankunan da manomansu suka amfana da shirin tallafawa bunkasar ayyukan nom ana Ancho Borrower da aka kaddamar a karkashin jagorancin babban bankin kasar CBN fiye da shekaru 3 da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.