Isa ga babban shafi
Najeriya - Kaduna

Yadda wata mujami'ar kiristoci ta tallafa wa musulmai da kayan sallah a Kaduna

A Najeriya, yayin da ake shirin gudanar da bukukuwan Sallah karama, Wata Mujami'a a jihar Kaduna ta rabawa marayu 100 maza da mata kayan Sallah domin faranta ma su rai.

Fasto Yohanna YD Buru da ya jagoranci rabawa marayu kayan sallah a jihar Kaduna
Fasto Yohanna YD Buru da ya jagoranci rabawa marayu kayan sallah a jihar Kaduna © pastor Yohanna YD Buru
Talla

A duk shekara musulmi a fadin duniya na gudanar da bikin sallah bayan kammala azumin watan Ramadan, Sai dai Marayu na shiga cikin halin kunci sakamakon rashin iyaye da zasu yi masu hidima musammam ma a irin wannan lokaci.

Marayun da suka samu tallafin kayan sallah daga wata Mujam'ar jihar Kaduna a Najeriya da Fasto Yohanna YD Buru da ya jagoranci rabawa
Marayun da suka samu tallafin kayan sallah daga wata Mujam'ar jihar Kaduna a Najeriya da Fasto Yohanna YD Buru da ya jagoranci rabawa © Pastor Yohanna YD Buru

A bisa la'akari da irin wannan halin kunci da marayu ke shiga yasa wata Mujami'a a jihar Kaduna karkashin jagorancun Fasto Yohana Buru rabawa marayu maza da mata guda 100 kayan sawa  domin ta faranta ma su rai adaidai lokacin da za'a gudanar da bikin sallah.

Yadda wata mujami'ar kiristoci ta tallafa wa musulmai da kayan sallah a Kaduna
01:31

NIGERIA-KADUNA-AMINU-SADO-2021-05-12

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.