Zan kawo karshen 'yan bindiga a Zamfara cikin kwanaki 4 - Matawalle
Gwamnan jihar Zamfara a Najeriya ya lashi takobin murkushe 'yan bindiga cikin kwanaki hudu tare da kawo karshen muggan ayyukansu a fadin jihar.
Wallafawa ranar:
Gwaman Bello Matawalle Muradun ya bayyana haka ne lokacin da ya karbi bakwancin shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC karkashin jagorancin Gwamnan jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu da takwaransa na Jigawa Abubakar Badaru a wani ziyarar jaje da suka kai Gusau.
Gwamna Matawalle ya gargadi 'yan bindiga a jihar da su tuba ko su sauya sheka domin ya tsara sabon tsarin yadda zai tunkari matsalar kalubalen tsaro da jihar ke fuskanta.
Ya ce dakatarwar da ya yi wa wani hakimi a masarautar Shinkafi kwanan nan saboda mu’amala da 'yan ta'adda somin tabi ne, yana mai cewa a cikin kwanaki hudu masu zuwa, zai shawo kan duk wadanda ke sanya rayuwar al’umma da basu ji ba basu gani ba cikin kuncin rayuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu