Isa ga babban shafi
Najeriya-Neja-Zamfara

'Yan bindiga sun saki daliban Kagara kwanaki 10 bayan yin garkuwa da su

‘Yan bindiga a Najeriya sun saki daliban makarantar sakandaren Kagara 27 da kuma malamansu da wasu ma’aikata 15 da suka sace kwanaki 10 da suka gabata a jihar Neja.

Daliban makarantar Sakandaren garin Kagara da 'yan bindiga suka saki bayan shafe kwanaki 10 suna garkuwa da su.
Daliban makarantar Sakandaren garin Kagara da 'yan bindiga suka saki bayan shafe kwanaki 10 suna garkuwa da su. AP
Talla

A tsakiyar watan Fabarairun da muke gungun ‘yan bindiga sanye da kakin sojoji suka kutsa makarantar sakandaren ta Kagara inda suka yi awon gaba da mutane 42, da suka hada da dalibai 27 da malamai da wasu ma’aikata 15, bayan da suka kashe dalibi guda 1 da yayi kokarin tserewa.

Yayin tabbatar da sakin daliban ta shafinsa na twitter, gwamnan jihar ta Neja Abubakar Sani Bello yace tuni ya karbi bakuncin jumillar mutanen 42 a garin Minna.

Gwaman jihar Neja a Najeriya Abubakar Sani Bello yayin da ya karbi bakwancin daliban sakandaren garin Kagara da yan bindiga sukayi garkuwa da su

Sakin daliban na Kagara na zuwa ne, a yayinda hankula suka tashi a ciki da wajen Najeriyar, biyo bayan sace dalibai 317 da wani gungun ‘yan binidgar suka yi daga makarantar ‘yammata ta Jengebe dake jihar Zamfara, wadanda hukumomin tsaro suka bazama wajen kokarin ceto su.

Wata daliba da ta tsallake rijiya da baya yayin da 'yan bindiga suka sace dalibai sama da 300 daga makarantar sakandaren 'yammata ta Jangebe dake jihar Zamfara a arewacin Najeriya.
Wata daliba da ta tsallake rijiya da baya yayin da 'yan bindiga suka sace dalibai sama da 300 daga makarantar sakandaren 'yammata ta Jangebe dake jihar Zamfara a arewacin Najeriya. AP - Ibrahim Mansur

Tuni dai gwamnatin Zamfara ta bada umarnin rufe ilahirin makarantun kwanan dake jihar, domin dakile yunkurin sake kai farmakin sace dalibai, matakin da ita ma gwamnatin Kano ta dauka, inda ta garkame wasu makarantun kwanan dake kauyukan jihar.

Hare-haren ‘yan binidga da satar mutane a yankin arewa maso yammacin Najeriya na cigaba da yin kamari a baya bayan nan, duk da ikirarin gwamnati na daukar matakan kawo karshen matsalar da suka hada da murkushe barayin da karfin jami’an tsaro, tare da mika musu tayin sulhu a matakan wasu jihohi.

A shekarar bara wasu gungun ‘yan binidgar suka sace dalibai sama da 200 daga makarantar sakandaren kimiyya ta Kankara da ke jihar Katsina, wadanda aka sako su bayan shafe kusan mako guda ana garkuwa da su.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.