Isa ga babban shafi

Ba shiga ba fita a Daura- Gwamnan Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina da ke arewacin Najeriya ta kafa dokar hana shige da fice  a Karamar Hukumar Daura bayan gano wasu karin mutane dauke da cutar coronavirus, lamarin da ke zuwa jim kadan da mutuwar wani likita a sanadiyar cutar.

Gwamnan jihar Katsina Amnu Bello Masari
Gwamnan jihar Katsina Amnu Bello Masari freedomradionig
Talla

Gwamnan jihar, Aminu Bello Masari ya ce, dokar hana shige da ficen za ta fara aiki ne daga karfe bakwai na safiyar Asabar (wato gobe) a garin na Daura bayan gano mutane uku da suka kamu da cutar.

Mutanen da aka gano sun kamu da cutar, iyalan likitan nan ne da coronavirus ta kashe shi a garin.

Kuna iya latsa alamar sautin da ke kasa domin sauraren bayanin Gwamna Aminu Bello Masari

00:46

Muryar Aminu Bello Masari kan dokar hana fita a Daura

Jim kadan da mutuwarsa ne aka yi wa iyalansa gwaji, inda sakamako ya nuna cewa, lallai sun harbu da annobar.

A cikin makon nan ne, gwamna Masari ya sanar cewa coronavirus ce ta yi ajalin likitan bayan ya dawo daga jihohin Kogi da Lagos.

A karo na farko kenan da cutar coronavirus ke kisa a Jihar Katsina.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.