Coronavirus ta kashe likita a jihar Katsina
Wani likita a Daura da ke jihar Katsinan Najeriya ya mutu sakamakon kamuwa da cutar coronavirus, bayan ya ziyarci jihohin Kogi da Lagos.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Gwamnan Jihar Aminu Bello Masari ya sanar da mutuwarsa bayan an yi gwajin samfurin jininsa a birnin Abuja wanda ya tabbatar cewa cutar ta coronavirus ta kashe shi.
Kuna iya latsa alamar sautin da ke kasa domin sauraren cikakken bayanin da gwamnan Katsina ya yi kan mutuwar likitan.
Aminu Bello Masari kan mutuwar likita a Daura bayan fama da coronavirus
Masari ya ce, tuni suka tashi tawagar likitoci zuwa garin Daura domin bin diddigin mutanen da likitan ya yi hulda da su da zummar yi musu gwaji da kuma killace su saboda fargabar cewa, su ma sun kamu da wannan annoba.
Ana iya cewa wannan ne karo na farko da cutar coronavirus ke kisa a Jihar Katsina da ke Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu