Isa ga babban shafi
Coronavirus

Yawan wadanda suka kamu da Coronavirus a Najeriya ya kai 30

Gwamnatin Najeriya tace adadin mutanen da suka kamu da cutar coronavirus yak ai 30 a fadin kasar, bayan samun karin mutane 3 da suke dauke da ita a Lagos.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari. AFP
Talla

Ma’aikatar lafiyar Jihar Lagos tace cikin sabbin mutane 3 da aka samu dauke da cutar akwai dan Birtaniya da ya shiga Najeriya ranar 8 ga wata da wani dan Najeriya da ya koma gida daga London sai kuma wani BaAmurke da yaje kasar makwanni 6 da suka gabata.

Yayin jawabi na farko da ya gabatarwa al'ummar kasar, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yace gwamnatinsa daukar matakan da suka dace domin kare lafiyar al’ummar kasar.

00:27

Jawabin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari kan annobar Coronavirus

Nura Ado Suleiman

A wani labarin kuma gwamnatin makwabciyar Najeriya, wato Jamhuriyar Nijar ta tabbatar da samun mutumi na biyu da ya kamu da cutar coronavirus, bayan wanda aka samu na farko a makon jiya.

Ministan lafiya Dr Ilyasu Idi Mainasara yace wani dan kasar Italia aka gano yana dauke da cutar.

00:39

Ministan lafiyar Jamhuriyar Nijar Dakta Ilyasu Idi Mainasara

Nura Ado Suleiman

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.