Isa ga babban shafi
Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta yi wa sassanta garambawul

Rundunar sojin Najeriya, ta sanar da yin garambawul ga shugabancin sassanta, musamman rundunar ta da ke yakar kungiyar Boko haram ta 'Operation Lafiya Dole'.

Wasu jami'an sojin Najeriya.
Wasu jami'an sojin Najeriya. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Cikin sanarwar da kakakin rundunar sojin Najeriyar Birgediya Janar Texas Chukwu ya fitar, daga ranar 1 ga watan Agusta na 2018 da muke ciki, Manjo Janar Abba Dikko, zai maye gurbin Manjo Janar Rodgers Nicholas a matsayin sabon kwamandan rundunar Operation lafiya dole.

Sai kuma Manjo Janar C.O Ude da zai maye gurbin Manjo Janar Lucky Irabor, a matsayin sabon kwamandan rundunar hadin gwiwar kasashen da fama da rikicin Boko Haram da ke Hedikwata a Ndjamena, babban birnin kasar Chadi.

Sauye-sauyen sun zo ne, makwanni biyu ko kasa da haka, bayan hare-haren da mayakan Boko Haram suka kai kan sansanonin sojin Najeriya da ke Bama a jihar Borno da kuma Jilli a Yobe.

Zalika a lahadin da ta gabata, wasu dakarun Najeriyar da ke karamar hukumar Tarmuwa sun tsira daga wani kwanton bauna da mayakan na Boko sukai musu.

A baya bayan nan dai rundunar sojin Najeriya ta samu nasarori da dama kan mayakan Boko Haram, wanda hakan ya rage karfin kungiyar ta yadda a mafi akasarin lokuta ta ke amfani da 'yan kunar bakin wake, wajen kai hare-hare, a maimakon samamen da takan kai a baya, inda ta ke yin nasarar kwace wasu yankuna a shekarun baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.