Rundunar Sojin Najeriya ta musanta bacewar jami'anta
Rundunar Sojin Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa, dakarunta da motocinta sun bace bayan wani hari da kungiyar Boko Haram ta kaddamar mu su a garin Bama da ke jihar Borno.
Wallafawa ranar:
Sanarwar da darektan hulda da jama’a na rundunar, Birgediya Janar Texas Chukwu ya fitar a ranar Litinin ta ce, babu kamshin gaskiya a labarin bacewar jami’an.
A cewar Chukwu, babu shakka ‘yan ta’adda na Boko Haram sun far wa sojojin a Kwakwa da Chingori da ke Bama, in da suka yi kokarin awon gaba da motocin dakarun amma aka fatattake su.
Mr. Chukwu ya kara da cewa, an yi nasarar kwance damarar mayakan Boko Haram 22, yayin da dama daga cikinsu suka samu rauni.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu