Babachir na ba mu haɗin kai-EFCC
Hukumar yaƙi da rashawa da yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon ƙasa EFCC ta kame tsohon sakataren gwamnatin tarayyar ƙasar Mista Babachir Lawal.
Wallafawa ranar:
Yayin da yake tabbatar wa manema labarai tsare tsohon sakataren gwamnatin, kakakin hukumar EFCC Samin Amaddin ya ce, Babachir na ba su haɗin kai dangane da ƙarin bayanan da suke nema, waɗanda suka shafi binciken da a ke yi a kansa.
A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kori sakataren gwamnatin tarayyar Babachir Lawal bayan kammala binciken kwamitin da aka kafa kan zargin sa da karya dokar kasa wajen bai wa kamfaninsa kwangilar cire ciyawa a jihar Yobe a kan kudi Naira miliyan 200.
Ƙungiyoyin fararen hula da yan adawa sun sha zargin Muhammadu Buhari da gazawa ko kuma nuna son kai wajen hukunta masu hannu a ayyukan rashawa a ƙasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu