Gwamnatin Najeriya ta ce kuskure aka samu wajen nadin matattu
Gwamnatin Najeriya ta kare kanta daga zargin cewa rashin iya aiki ne ya sanya bayyanar sunayen mutanen da suka mutu a jerin sabbin nade-nade na mutane dubu 1,258 da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi, na shugabannin hukumomin gwamnatin kasar da sauran ma’aikatu.
Wallafawa ranar:
Kakakin shugaban Najeriya Malam Garba Shehu, ya ce an zabo mutanen ne, tun kafin shugaba Muhammadu Buhari ya kwanta Jiyya, sai dai ba’a bayyana wadanda aka nada bisa sabbin mukaman ba, saboda yadda wasu kusoshin gwamnatin suka yi, ciki harda gwamnoni.
Daga baya ne kuma aka wallafa sunayen ba tare da an sake bibiyarsu ba.
Daga cikin sunayen matattun da suka bayyana akwai tsohon mataimakin Sifeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Francis Okpozo, wanda ya mutu tun a watan Disamba na shekara ta 2016.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu