Isa ga babban shafi
Najeriya

Kotun Najeriya ta ayyana IPOB a matsayin ta 'yan ta'adda

Babbar kotun tarayya da ke birnin Abuja ta bada umarnin ayyana kungiyar masu fafatukar kafa kasar Biafra, IPOB a matsayin ta ‘yan ta’adda

Masu fafutukar kafa kasar Biafra a yankin kudancin Najeriya
Masu fafutukar kafa kasar Biafra a yankin kudancin Najeriya STEFAN HEUNIS / AFP
Talla

Kotun ta bada umarnin ne bayan ministan shari’a kuma lauyan gwamnati, Abubakar Malami ya shigar da batun a gabanta a madadin gwamnatin tarayya.

Kotun ta kuma haramta ayyuakn kungiyar a dukkanin fadin Najeriya musamman a yankunan kudu maso gabashi da kudu maso kudu, in da masu fafutukar suka fi tayar da kayar baya.

Gabanin wannan matakin na kotun, rundunar sojin kasar ta ayyana kungiyar IPOB a matsayin ta ‘yan ta’adda, amma ta sha suka daga wasu bangarori da ke cewa, rundunar ba ta bi ka’ida ba kafin ayyana kungiyar a matsayin ta ‘yan ta’adda.

A bangare guda, gwamnatin Najeriya ta zargi cewa, masu fafutukar kafa Biafra na samun tallafin kudade daga kasashen waje.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.