Damben gargajiya daga jihar Kaduna
A wasan damben gargajiya da a ka fafata jiya da yammacin Litini a gidan damben Umaru Fiyalu da ke Kaduna Najeriya John Sina daga bangaren Arewa ya doke Dan Hausa daga bangaren kudu.
Wallafawa ranar:
Shagon Audu Argungu daga bangaren Arewa ya buge Kurarin Ja’afaru.
Wasannin da aka tashi ba kisa sun hada da :
Damben Dan Ananu daga bangaren kudu da Bahagon Dan Jamilu daga bangaren Arewa.
Na biyu dambe tsakanin Shagon Dan Inda daga bangaren Arewa da Shagon bata isakka daga bangaren kudu.
Na karshe damben da aka fafata tsakanin Bahagon Sisco daga kudu da kumaTula daga bangaren Arewa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu