Ilimi Hasken Rayuwa
Rawar da wata cibiya ta taka wajen samar da makamashi a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:03
Shirin ilimi hasken rayuwa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya kai ziyara ne a cibiyar kera kayayyakin samar da makamashin wutar lantarki mai amfani da hasken rana. Cibiyar ta kwashe sama da shekaru 30 ta na gudanar da bincike kan samar da makamashi kuma ta samu gagarumar nasara a wannan fanni. Sai dai akasarin 'yan Najeriya ba su da masaniya game da wannan cibiya.