Isa ga babban shafi
Najeriya

Ma'aikatan kwadago na yajin aiki a Arik Air

Kungiyoyin kwadago da ke bangaren sufurin jiragen sama sun yi barazanar durkusar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Arik daga yau Talata saboda abin da suka kira kasa biyan albashin watanni 7 da kuma dawo da ma’aikatan da aka kora daga aiki. 

Jirgin sama na kamfanin Arik
Jirgin sama na kamfanin Arik Crédit : Biggerben/Wimedia Commons
Talla

Sanarwar da shugabanin kungiyoyin suka gabatar, cikin su har da matuka jiragen da injiniyoyi, ta nuna cewar yajin aikin nasu zai ci gaba har illa Masha-Allahu, matukar kamfanin bai biya hakkokin ma'aikatan ba.

Yajin aikin ba karamar illa zai yi wa matafiya a Najeriya ba, musamman a wannan lokaci na tafiya hutu, ganin cewar kamfanin ne mafi girma a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.