Majalisar Najeriya ta yi wasti da nadin Magu a EFCC
Majalisar Dattawan Najeriya taki amincewa da nadin Ibrahim Magu a matsayin shugaban hukumar EFCC da ke yaki da cin hanci da rashawa a kasar.
Wallafawa ranar:
Majalisar ta sanar da haka ne yau Alhamis bayan wani zama da ta yi na tantance shugaban kamar yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gabatar da sunan sa.
Mai Magana da yawun Majalisar Aliyu Sebi ya danganta matakin su da bayanan asiri da ya ce sun samu.
Masu sa'ido na kallon matakin a matsayin wani yunkuri na zagon kasa ga yaki da cin hancin ganin cewar wasu daga cikin 'yan majalisun yanzu haka suna fuskantar tuhuma daga hukumar a gaban kotu saboda rub da ciki da kudaden talakawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu