Buhari ya nada Mustapha Magu shugaban EFCC
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada Ibrahim Mustapha Magu a matsayin shugaban hukumar EFCC da ke yaki da masu yi wa tattalin arziki zagon kasa, wanda ya maye gurbin Ibrahim Lamorde da aikin sa zai kare a watan Fabarairu mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Sanarwar da Femi Adeshina mai bai wa Buhari shawara kan harkokin yada labarai ya fitar, ta nuna cewar Magu na cikin ‘yan kwamitin da ke ba shugaban shawara kan yadda za a inganta yaki da cin hanci da rashawa a fadin Najeriya
Sanarwar tace Magu ya taba aiki a hukumar EFCC a karkashin Nuhu Ribadu kuma ya jagoranci binciken da suka hada da rugujewar Societe General Bank da kuma tsohon Gwamnan Delta James Ibori.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin magance matsalar Yaki da cin hanci da Rashawa a Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu