Najeriya ta lashe gasar Afrika ta mata
Babbar kungiyar kwallon kafa ta Najeriya ta lashe gasar cin kofin nahiyar Afrika ta mata da aka gudanar a Jamhuriyar Kamaru.
Wallafawa ranar:
Kungiyar ta Super Falcons ta samu nasarar ce bayan da ta doke takwararta ta Kamaru, Indomitable Lionesses da ci daya mai haushi a wasan karshe da suka fafata a filin wasa na Ahmadou Ahidjo da ke birnin Younde.
Desire Oparanozie ce ta jefa kwallon tilo da ta bai wa Najeriya nasara.
Tuni dai shugaban kasar, Muhammadu Buhari ya jinjina wa Super Falcons bisa wannan nasarar da ta samu a yau Aasabar.
Shugaba Buahri ya bayyana nasarar a matsayin abin farin ciki, yayin da a karo na takwas kenan da Najeriyar ke lashe wannan kofin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu