An yiwa Sarkin Musulmi Kasaitacciyar Durbar a Najeriya
Yau Dubban mutane ne daga sassa dabam dabam suka halarci wata kasaitacciyar durbar da aka yiwa Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Muhammad Saad Abubakar na 3 wanda ya cika shekaru 10 a karagar mulki.
Wallafawa ranar:
Bikin ya samu halartar Shugaban kasar Muhammadu Buhari da Gwamnonin Jihohi da Sarakuna daga sasan Najeriya da kasashen waje.
Sarakuna da masu rike da Sarautar a Masaarutar Sokoto sun yi hawa idan suka sake jaddada mubayi’ar su ga Sarkin Musulmi.
Cikin wadanda suka yi hawan harda tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Gwamnan Imo Rochas Okorocha da Bishop Mathew Hassan Kukah.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu