Isa ga babban shafi
Najeriya

Kungiyoyi sun yi tayin taimakawa a tattauna da Boko Haram

Wasu kungiyoyi sun yi tayin taimakawa gwamnatin Najeriya, wajen tattaunawa da mayakan Boko Haram, domin musayar ‘yan makarantar Chibok da suke rike da su, da kuma wasu daga cikin fursunonin mayakan.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari sanye da kakin Soja
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari sanye da kakin Soja saharareporters
Talla

Mai bawa shugaban Najriyar shawara kan kafafen yada labarai malam Garba Shehu ne ya tabbatar da hakan a zantawarsa da manema labarai.

Cigaban na zuwa ne bayan da shugaban Najeriyar Muhdu Buhari, a lokacin wani taro a kasar Kenya watan da ya gabata, ya ce a shirye Najeriyar ta ke, ta tattauna da Mayakan ta hanyar wakilcin manyan kungiyoyin kasa da kasa daga bangaren Boko Haram din.

Wani masani kan yaki da ta’addanci a Najeriyar dakta Ameachi Nwoakolo, ya ce musayar ‘yan matan da fursunonin mayakan bai sabawa ka’aida ba, kasancewar mataki ne da dukkan kasashen duniya ke dauka.

Yanzu dai lokaci ne zai nuna tabbatuwar fara wannan tattaunawa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.