Najeriya za ta ci gaba da fama da karancin mai
Ministan kasa a ma’aikatar mai ta tarayyar Najeriya Ibe Kachikwu, ya ce za a ci gaba da fuskantar matsalar mai a kasar har nan da watanni biyu masu zuwa.
Wallafawa ranar:
Mr.Kachukwu ya bayyana haka ne bayan wata ganawa da aka yi a jiya tsakanin shugaban kasar Muhammadu Buhari da kungiyoyin ma’aikatan mai na kasar.
Ministan ya ce, an fuskanci matsaloli ta fannin samar da mai a cikin gida, lamarin da ya sa ana shigo da man kashi 100 bisa 100 daga waje a maimakon kashi 50 cikin dari.
A duk lokacin da aka samu karancin mai dai, al'ummar Najeriya na kokawa saboda matsanancin halin da suke samun kan su a ciki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu