Nigeria
'Yan Sanda a Lagos sun Kubutar da "Yan Mata uku da aka Sace Daga Makaranta
‘Yan Sanda a jihar Legas dake Nigeria sun yi nasarar kubutar da wasu ‘yan mata uku ‘yan makarantar Sakandare na kwana da aka sace su makon jiya.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin ‘Yan Sanda na jihar Legas Dolapo Badmus ta shaidawa kamfanin Dillancin labaran Faransa cewa kafin wayewar gari yau lahadi aka kubutar da ‘yan matan.
‘Yan matan uku na Makarantar Sakandare na Babington Macaulay ne dake yankin Ikorodu.
Babu wasu bayanai gameda ko an biya wasu kudade ne kafin a kubutar da ‘yan matan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu