CAF
Najeriya ta tsallake zuwa gasar Afrika a Rwanda
Najeriya ta tsallake zuwa gasar Afrika ta matasa da ke taka kwallo a gida da za a gudanar a Rwanda a badi, bayan ta rike Burkina Faso babu ci a Ouagadougou.
Wallafawa ranar:
Talla
Najeriya ta samu nasarar tsallakewa ne saboda nasarar kwallaye biyu ta zira a ragar Burkina a karawa ta farko.
Kasashen da suka tsallake gasar sun hada da Rwanda mai masaukin baki da Morocco da Tunisia da Mali da Guinea da Nijar da Gabon da Jamhuriyyar Congo da Uganda da Habasha da Zimbabwe da Zambia da kuma Angola.
A 16 ga watan Janairun 2016 ne za a fara bude gasar a kuma a 7 ga watan Fabrairu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu