Isa ga babban shafi
Najeriya

Ban Ki-Moon ya isa Najeriya

Sakatare Janar na Majasar Dinkin Duniya, Ban Ki-Moon ya isa Kasar Najeriya a yammacin yau lahadi domin tunawa da ranar da Kungiyar Boko Haram ta kai harin Bam a Ofishin Majalisar dake birnin Abuja  shekaru uku da suka gabata.

Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon
Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon REUTERS/Kim Hong-Ji
Talla

Da misalin karfe hudu agogon Kasar ne, Mr. Ban ya sauka a filin jiragen Sama na Abuja yayin da kuma ake kyautatata zatan cewa zai tabo batun yaki da ta’addanci a tattaunawar da zai yi da Shugaba Muhammadu Buhari.

Kana Mr. Ban zai sanya fure, domin tunawa da cika shekarau 4 da harin wanda ya kashe mutane 21 a wancan lokacin a Ofishin Majalisar.

Tun bayan da Shugaba Buhari ya karbi madafun ikon kasar, ake ci gaba da yakar mayakan na Boko Haram, da kawo yanzu suka hallaka dubun dubatar mutane a kasashen yammacin Afrika da suka hada da Najeriya, Nijar, Kamaru da Chadi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.