Isa ga babban shafi
Najeriya

Amnesty ta damu da kisan mutane da Boko Haram suka yi a Baga

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty ta tabbatar da harin da mayakan kungiyar book haram suka kai a garin Baga na jihar Borno a Nigeria, inda suka kashe a kalla mutane dubu 2

Vifusi vya nyumba katika mji wa Bama, kaskazini-mashariki mwa Nigeria baada ya mashambulizi yaliyotekelezwa na Boko Haram, Februari mwaka 2014.
Vifusi vya nyumba katika mji wa Bama, kaskazini-mashariki mwa Nigeria baada ya mashambulizi yaliyotekelezwa na Boko Haram, Februari mwaka 2014. AFP PHOTO / STRINGER
Talla

Kungiyar ta ce ta sami tabbacin hakan ne ta hanyar hotunan da ta samu daga tauraron dan Adam.

Cikin sanarwar da ta fitar kungiyar ta Amnesty tace tayi binciken ta ne kan 2 daga cikin garuruwa da dama da mayan na Boko Haran suka far wa.

Hotunan da kungiyar ta Amnesty ta fitar sun nuna yadda mayakan suka yi fata fata da garin Baga da Doron Baga, inda aka ga gine gine kusan dubu 4 a lalace. Suma sauran garuruwan dake gewaye da garin basu tsira daga harin ba.

Wani mutum mai shekaru 50 da wani abu da kungiya ta ji bahasi daga gare shi, yace an kashe mutane da dama yayin harin na makon daya gabata, inda shi da sauran mutane suka tsere, mayakn suna kai musu harbi.

Wani mutumin yace mayakan na Boko Haram suna harbi kan mai uwa da wabi, inda suka kashe mutanen da suka hada da yara kanana.

Kungiyar ta bayyana takaicinta kan yadda jami’an tsaro basa yin abinda ya dace, don kare fararen hula daga cin zarafin da ‘yan book Haram din ke yi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.