Najeriya na dab da tsallakewa zuwa gasar cin Kofin Duniya a Brazil
Kasar Malawi ta bude wa Najeriya kofar tsallakewa zuwa gasar cin kofin Duniya a Brazil bayan sun tashi wasa ci 2-2 da Kenya. Tazarar maki daya ne yanzu Najeriya ta ba Malawi a rukuninsu na F, amma tazarar za ta koma maki hudu idan har ‘Yan wasan Super Eagles suka samu nasarar doke Namibia idan an jima.
Wallafawa ranar:
Idan dai Najeriya ta samu nasara za ta kasance kasa ta farko daga Afrika da ta tsallake zuwa gasar cin kofin duniya da za’a gudanar a badi a kasar Brazil.
Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da Najeriya ke shirye shiryen shiga gasar cin kofin zakarun Nahiyoyin Duniya da za'a fara karawa a karshen makon a Brazil.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu