'Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu ‘yan kasashen waje a Najeriya
Rahotanni daga Najeriya na nuna cewa wasu ‘Yan bindiga suna garkuwa da wasu ma’aikata su bakwai ‘yan kasar waje wanda ke aiki a wani kamfani dake garin Bauchi mallakar wani dan kasar Lebanon, cikinsu har da wani dan kasar Girka. A yayin yin garkuwa da mutanen, daya daga cikin masu tsaron kamfanin ya rasa ransa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ofishin jakadancin kasar Girka dake Najeriya ya tabbatar da aukuwar wannan lamarin inda bayyana yin garkuwan da daya daga cikin ‘yan kasarsa.
Kamfanin wanda akewa lakabi da SETRACO yana karamar hukumar Jama’are ne a Jihar ta Bauchi, a yayin da tuni ofishin jakadancin kasar ta Girka ya sanar da iyalan dan Girkan da ake garkuwa da shi.
Wasu daga cikin ‘yan kasashen wajen da ake garkuwan da su, sun hada da wani dan kasar Italiya da kuma dan kasar ta Lebanon.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu