Nigeria
David Cameron ya nemi karfafa kasuwanci tsakanin Africa da Britaniya
Prime Ministan kasar Britaiya David Cameron, ya nemi a kara karfafa harkin cinikayya tsakanin kasar shi da sauran kasashen nihiyar Africa. Mr Cameron da ke magana a yau yayin wata ziyarar da ya kai Nigeria, inda ya ce nahiyar Africa nahiya ce da ya kamata a tallafa mata, amma kuma waje da ya kamata a yi huldar kasuwanci da ita, amma kuma kafin nan ya kamata a samar da gyare- gyare a harkokin siyasa, kafin kuma a samar da wannan sai an sami ginshikan democradiyya, kamar su bin doka da oda sakar wa bangaren shari’a mara, da kuma gwamnatin democradiyya da ba rufa rufa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: