‘Yan sandan Amurka sun tabbatar da mutuwar mutumin da ya kashe yara 20
‘Yan sanda a kasar Amurka sun tabbatar da mutuwar mutumin nan da ya kasha yara kanana 20, da manya 6, a wata makarantar Piramare a jihar Connecticut, da cewa sunan shi Adam Lanza, mai shekaru 20.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
‘Yan sandan sun kuma bayar da tabbacin cewa matashin ya kashe kanshi ne bayan aika-aikar, da ya faro da kashe mahaifiyar shi, mai suna Nancy, a gidan su, bayan da ya yi ta harbin ta.
Wani jami’in ‘yan sanda mai suna Paul Vance, ya ce Lanza ya harbi kan shi da wata karamar bindiga, sai dai bai bayyana dalilan da suka sa Lanza ya aikata ta’asar ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu