Serbia
An Kama Ratko Mladic Na Bosnia Da Ake Nema
Shugaban Serbia Boris Tadic ya bayyana kama tsohon Kwamandan Sojan kasar Ratko Mladic wanda aka dade ana nema ruwa a jallo saboda laifukan yaki.Shugaban kasar ya fadawa taron manema labarai yau cewa da safe aka kama shi kuma ana tsara yadda za'a tasa keyarsa zuwa kotu kasa-da-kasa dake hukunta masu aikata laifukan yaki dake Hague.Ana zargin Ratko Mladic ne da laifin kisan kiyashi tsakanin shekarar 1992-1995 lokacin rugujewar kasar YugoslaviaMai shekaru 69 ana zargin sa da kafa sansanoni da wuraren tsare mutane da kisan jama'a.
Wallafawa ranar: