Isa ga babban shafi

Dakarun Isra’ila sun kama darakta asibitin Gaza na Al-Shifa

Wani likita a babban asibitin Gaza Al-Shifa ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa dakarun Isra'ila sun kama daraktan cibiyar da wasu ma'aikatan lafiya da dama a yau Alhamis.

Marar sa lafiya a asibitin  Al-Shifa, na Gaza
Marar sa lafiya a asibitin Al-Shifa, na Gaza AFP - KHADER AL ZANOUN
Talla

Daraktan asibitin mai suna Mohammad Abu Salmiya na daya daga cikin mutanen da Isra;ial ke kalo a matsayin Wanda ke sanar da Duniya halin da ake ciki  a duk lokacin da aka samu mutanen da suka jikkata ko suka mutu biyo vayan harin dakarun Isra’ila yankin na Gaza.

A daya gefen sojojin Isra'ila da suka kai samame asibitin a makon da ya gabata, sun yi zargin cewa mayakan Hamas sun yi amfani da wani rami da ke karkashin cibiyar a birnin Gaza wajen kai hare-hare.

Zargin da kungiyar Hamas da jami'an asibiti suka sha musantawa.

Asibitin Al-Shifa, a Gaza
Asibitin Al-Shifa, a Gaza © Capture d'écran/ Montage RFI

Khalid Abu Samra, shugaban sashen asibitin ya sheidawa manem alabarai cewa ‘’an kama Dakta Mohammad Abu Salmiya tare da wasu manyan likitoci,"kuma nan take kungiyar ta Hamas  ta yi Allah-wadai da kamun da aka yi ma’aikatan asibitin, tana mai kira ga kungiyar agaji ta Red Cross da sauran kungiyoyin kasa da kasa da su yi kokarin ganin an sako su cikin gaggawa.

Wasu daga cikin jarirai a asibitin Rafah, a yankin Gaza
Wasu daga cikin jarirai a asibitin Rafah, a yankin Gaza REUTERS - IBRAHEEM ABU MUSTAFA

A ranar Asabar da ta gabata ne ,dakarun Isra’ila suka  bayar da umarnin ficewa daga asibitin , lamarin da ya sa daruruwan majinyata ke gudun hijira tare da yin kaura zuwa kudancin Falasdinu.

Domin wanke kansu daga duk wani zargin cin zarrafi,dakarun Isra’ila sun fitar da wani faifan  murya ,wanda ke tabbatar da zargin da  Isra'ila ke yi cewa Hamas na gudanar da wata cibiyar ba da umurni a cikin ramukan da ke ƙarƙashin asibitin na tsawon shekaru - zargin da ƙungiyoyin Hamas da ma'aikatan lafiya suka fatali da shi.

Wasu da suka cira daga harin Isra'ila
Wasu da suka cira daga harin Isra'ila AP - Hatem Ali

A ranar Laraba, sojojin Isra'ila sun raka 'yan jarida zuwa daya daga cikin  ramin  da suka ce wani bangare ne na wata babbar hanyar sadarwa ta karkashin kasa da Hamas ke amfani da shi.

Asibitin Al-Shifa dai ya kasance wurin da dakarun Isra'ila suka kara kai farmaki a wani bangare na yakin da suke yi da kungiyar Hamas a zirin Gaza, inda gwamnatin Hamas ta ce an kashe fiye da mutane 14,000 wadanda yawancinsu mata da yara ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.