Isa ga babban shafi

Mutane 2 sun mutu a wani harin da aka kai ofishin jakadancin Amurka a Saudiya

Mutane 2 da suka hada da wani mahari  sun mutu a cikin wata musayar wuta da ta faru a jiya Laraba a gaban karamin ofishin jakadancin Amurka dake birnin Jiddah na Saudiyya, kamar yadda mahukuntan masarautar suka sanar. 

Tutar kasar Saudiya
Tutar kasar Saudiya REUTERS - HUSEYIN ALDEMIR
Talla

KamfanindillancinlabaranSaudiya SPA ya sanar da cewaMutumindakedauke da bindiga ya saukane daga cikinmotarsa a gabangininkafin a kasheshi a cikinwatamusayarwuta da jami’antsaro.

A cewarkakakinyansanda, wanijami’intsarodaya, dan asalinkasarNepal ya mutusakamakonraunin da ya samu. 

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ce babu wani dan kasarta da ya jikkata a ofishin jakadancinta, wanda aka takaita zirga-zirga a kewayensa.

A wata sanarwa, ma’aikatar ta mika sakon ta’aziyarta  ga iyalan mai gadin da  ya mutu a harin, inda ta ce tana tattaunawa da masarautar Saudiyyar, wadda ta kaddamar da bincike a kan lamarin.

Wannan harin na zuwa ne  daidai lokacin da Saudiyya ke karbar bakunci masu aikin hajji kusan miliyan biyu daga sassan duniya da ke sauke farali a birnin Makka, kilomita kusan 70 daga ofishin jakadancin Amurka.

Ofishin jakadancin Amurka ya fuskanci hare-hare a lokuta dabam dabam a shekarun baya, inda a ranar 4 ga watan Yuli ta shekarar 2016, wato ranar bikin samun yancin kan Amurka, wani dan kunar bakin wake ya tarwatse kansa a ofishin.

A watan Disamban shekarar 2004, wani hari ya yi   sanadin mutuwar mutane 5 a ofishin jakadancin na Amurka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.