Isra'ila ta kai farmaki kan cibiyoyin Hamas a Gaza
Jiragen yakin Isra'ila sun kai hari kan wasu cibiyoyin kera makaman sojojin Hamas dake Zirin Gaza a jiya Asabar, abinda rundunar sojin Isra’ilan ta bayyana a matsayin ramuwar gayya kan harba makamin roka cikin kasar daga yankin Falasdinu.
Wallafawa ranar:
Sanarwar ta ce, farmakin kan Gaza ya zo ne bayan da Hamas ta harba makamin roka kan fararen hular Isra'ila a kudancin kasar.
A ranar Asabar ne kuma, Isra'ila ta ce ta dakatar da baiwa karin ma’aikatan Falasdinawa izinin shiga cikinta daga yankin Gaza saboda harba mata makamin na roka da mayakan falasdinun suka yi.
Akalla Falasdinawa 12 suka jikkata a harin da sojojin Isra'ila suka kai a ranar Juma'a a Jenin, dake zama tungar kungiyoyi masu dauke da makamai a yammacin gabar kogin Jordan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu