Isa ga babban shafi
Iran - Isra'ila

Iran ta harba makamai masu linzami 16 yayin atasayen gargadi ga Isra'ila

Iran ta harba makamai masu linzami da dama a ranar Juma'a, rana ta karshe da ta gudanar da atasayen soji da ta shafe kwanaki 5 tana yi.

Iran ta yi atasayen harba makamai masu linzami domin gargadin kasar Isra'ila.
Iran ta yi atasayen harba makamai masu linzami domin gargadin kasar Isra'ila. © WANA (West Asia News Agency) / REUTERS
Talla

Manyan hafsoshin sojin kasar ta Iran dai sun bayyana atasayen a matsayin gargadi ga babbar abokiyar gabarsu Isra'ila.

Babban Hafsan sojojin Iran Manjo Janar Mohammad Bagheri, ya shaidawa gidan talabijin na kasar cewa, an tsara jerin atasayen ne domin mayar da martani ga barazanar da gwamnatin Isra’ila ta yi musu a baya bayan nan.

Janar Bagheri ya ce makamai masu linzami 16 da suka harba, kadan ne daga cikin daruruwan makamai masu linzami da Iran ta mallaka, wadanda za su iya amfani da su wajen kai hari kan dukkanin kasar da ta kuskura ta kai musu farmaki.

Sai dai, a wata sanarwa da ta fitar, ma'aikatar harkokin wajen Birtaniya ta yi Allah wadai da harba makamai masu linzamin da Iran ta yi, tana mai cewa hakan barazana ce ga tsaron yankin Gabas ta Tsakiya da ma duniya baki daya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.