Isa ga babban shafi
IRAN

Khamenei ya bukaci Iraniyawa su guji baiwa makiyarsu dama

Jagoran juyin - juya halin kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gargadi mazauna yankin da ke fama da fari a kudu maso yammancin kasar da kada su ba wa “makiya” dama, bayan kwashe kwanaki ana zanga-zangar da ta yi sanadiyar mutuwar akalla mutane hudu.

Jagoran juyin juya halin kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei.
Jagoran juyin juya halin kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei. AP
Talla

Yankin Khuzestan, babban yankin da Iran ke hako mai kuma mafi arziki a cikin larduna 31 na kasar, ya fada cikin fari tun daga watan Maris, inda zanga-zangar ta barke a garuruwa da biranen da dama tun ranar 15 ga watan Yulin.

Khamenei ya amince da tsananin matsalar da rashin ruwan sama ya janyo, ya kuma hakikance mazauna Khuzestan ba su da laifi don nuna rashin jin dadinsu, to amma ya bukace su da su yi taka tsantsan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.