Isa ga babban shafi
Najeriya-Kano

MOPPAN zata duba bukatar da Rahama Sadau ta mika mata

Fitacciyar Jarumar masana’antar fina-finan Hausa ta Kannywood Rahama Sadau, ta nemi afuwar hadaddiyar kungiyar masu ruwa da tsaki a harkar shirya fina-finan Hausa, MOPPAN, tare da neman kungiyar ta bata damar cigaba da haskawa a masana’antar.

Fitacciyar Jarumar Fina-finan Hausa Rahama Sadau.
Fitacciyar Jarumar Fina-finan Hausa Rahama Sadau. YouTube
Talla

Fitacciyar Jarumar ta nemi afuwar ce ta hanyar rubuta wasika zuwa ga shugabancin kungiyar ta MOPPAN, kamar yadda shaidar gani da ido, wato Jaridar Premium Times da ake wallafawa a Najeriya ta rawaito.

Yayin da yake amsa tambayar ko zasu amince da bukatar Jarumar, sakataren kungiyar ta MOPPAN Salisu Mohammed, ya ce zasu yi taro a ranar Juma’a 27 ga watan Oktoba, domin duba matakin da cancanta su dauka.

Idana za’a iya tunawa, a ranar 3 ga watan Oktoban shekara ta 2016, Hadaddiyar kungiyar ta masu ruwa da tsaki a harkar shirya fina-finan Hausa, MOPPAN ta dakatar da Rahama Sadau daga haskawa a fina-finan Hausa, sakamakon bidiyon wakar da yi, dawani mawaki Classiq, da suke rugumar juna.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.