Gobarar daji ta kashe mutane a kalla 51 a tsakiyar kasar Chille
Hukumomi a kasar Chili sun tabatar da mutuwar mitane 64 biyu bayan wuta daji data kama a tsakiyar kasar, kuma anasaran adadin mamatan ya karu a dai dai lokaci da yan kwana kwana ke fafutuka domin kashe wutar.
Wallafawa ranar:
Bakin hayaki ya mamaye sararin samaniyar yankin da gobaran dajin ta tashi ,yankin dake da mazauna sama da miliyan daya a tsakiyar kasar mai Gandun Daji, sai dai yan kwana kwana na anfani da jiragen sama da manyan motoci domin shawo kan gobara.
Yankin dake kusa da garin Vina da ake zuwa yawon shakatawa yanada tsananin zafi, a yayin da masu aikin jinkai ke karakaina dun cima inda wutar tayi barna, kamar yanda hukumomin kasar ta Chili suka bayyana.Ministan harkokin cikin Gidan kasar yace adadin mamatan na iya karuwa.
Wutar daji ba wani sabon abubane a kasar ta Chili, ko’a shekara data gabata saida mutane 27, suka rasa rayukansu tare ta kona komanin Hecters dubu dari 4. Yayin girgizar kasar da ta aukawa kasar a 2000 ta kashe mutane 500.
Daga rana Juma’a data gabata yankin da wutar dajin ta mamaye yakai fadin Hecters dubu 43, zuwa dubu dari da goma, daga dubu 30.
Ministan ya kara dacewa abunda mahukunta ke jima tsoro shine yanda wutar keci tana kara matsowa birane cikin gagawa inda ake saran zata farma gidaje da wasu kadarorin al’umma.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu