Isa ga babban shafi

Shugaban kasar Iran ya isa kasar Saudiya domin halartar wani taro kan Gaza

Shugaban kasar Iran Ibrahim Raïssi ya isa  Saudiya a yau Asabar domin halartar taron kasashen Larabawa da Musulunci kan yakin da ake yi tsakanin Isra'ila da kungiyar Hamas ta Falasdinu a zirin Gaza, kamar yadda kafar talabijin ta Al-Ekhbariya ta Saudiya ta sanar.

Shugaban kasar Iran Ebrahim Raïssi
Shugaban kasar Iran Ebrahim Raïssi AP - Vahid Salemi
Talla

Taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen Larabawa da musulmi na Duniya ya zo ne a wani lokaci da dakarun Isra'ila suka kashe mutane 11,000 galibi fararen hula da yawancinsu kananan yara, a cewar ma'aikatar lafiya ta Hamas.da dama a Gaza.

Shugabannin Gabas ta Tsakiya sun yi kira da a tsagaita wuta yayin da suke gargadin hadarin da ke tattare da rikici a wasu kasashe.

Shugaban Iran  Ebrahim Raïssi a kasar Saudiyya
Shugaban Iran Ebrahim Raïssi a kasar Saudiyya via REUTERS - WANA NEWS AGENCY

Hotunan da aka watsa a tashar Al-Ekhbariya sun nuna Shugaban Iran Raisi sanye da gyale na gargajiya na Falasdinu.

Saudiya mai rinjayen ‘yan Sunni da Iran mai rinjayen ‘yan Shi’a sun yanke alaka a shekarar 2016 bayan da aka kai wa ofisoshin jakadancin Saudiya hari a Iran a lokacin zanga-zangar nuna adawa da hukuncin kisa da Riyadh ta yi wa malamin Shi’a Nimr al-Nimr.

Taron kasashen Larabawa
Taron kasashen Larabawa REUTERS/Osman Orsal

Sai dai a watan Maris din da ya gabata, wata yarjejeniya da kasar Sin ta kulla, ya sa abokan hamayyar da suka dade suna adawa da juna sun amince da maido da huldar diflomasiyya tare da sake bude ofisoshin jakadancinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.