Zelensky ya zargi Rasha da cusawa yaran Ukraine tsananin kiyayyar kasar
Shugaba Volodymyr Zelensky, ya zargi Rasha da cusawa kananan yaran Ukraine da ta sace tsananin kiyayya ga kasarsu, tare da kawo karshen duk wata alaka da ‘yan uwansu na jini.
Wallafawa ranar:
Zelensky ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78 da ke gudana a birnin New York.
Fassarar kalaman shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky
Shugaban na Ukraine dai ya dade yana caccakar Rasha akan kwashe dubban kananan yaran da take yi daga yankunan kasarsa da ta kwace, lamarin da ya sa kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC ta bayar da sammacin a kamo mata shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu