Isa ga babban shafi

Ana zargin tsohuwar kungiyar FARC da dibar yara 18,000 cikin aikin soji

Wata kotu ta musamman ta kaddamar da bincike a kan tsohuwar kungiyar Yan Tawayen FARC dake kasar Colombia saboda zargin da ake mata na dibar yara kanana sama da 18,000 domin sanya su cikin aikin soji.

Wasu daga cikin Shugabanin kungiyar FARC
Wasu daga cikin Shugabanin kungiyar FARC AFP/File
Talla

A shekarar 2016 kungiyar ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya da gwamnatin, kuma daga cikin abinda bangarorin suka amince da shi harda kafa kotun bincike na musamman domin gano irin laifuffukan yakin da aka aikata.

Wasu daga cikin mayakan FARC
Wasu daga cikin mayakan FARC AP - Luis Benavides

Shugaban kotun na musamman Eduardo Cifuentes yace sanya kananan yara maza da mata cikin yakin ya yiwa al’ummar Colombia matukar illa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.