Za a rufe Masallacin Kudus a watan Ramadan
Majalisar da ke kula da Masallacin Birnin Kudus ko kuma Al-Aqsa, wanda shi ne na uku mafi daraja ga Musulmin duniya, ta ce za ta rufe Masallacin ga al’ummar Musulmi a lokacin azumin watan Ramadan mai zuwa saboda annobar coronavirus da ke ci gaba da lakume rayuka.
Wallafawa ranar:
Majalisar wadda ke karkahsin gwamnatin Jordan ta ce, daukar matakin ya biyo bayan shawarar da Majalisar Malamai da masana kiwon lafiya suka bayar.
Kodayake majalisar ta bayyana daukar wannan mataki a matsayin abin takaici, tana mai umartar Musulmai da su gudanar da sallolinsu da addu’o'insu a gida a cikin watan na Ramadan don kare lafiyarsu.
Sai dai za a ci gaba da kiran salla sau biyar a rana a Masallacin, sannan kuma za a bai wa ma’aikatan Masallacin damar shiga cikinsa.
Ana sa ran fara azumin Ramadan na bana a ranar 23 ga watan Afrilu da muke ciki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu