An bude taron kare muhalli na duniya a Kenya
Wakilan gwamnatoci, kamfanoni, cibiyoyin kudade da kuma kungiyoyi masu zaman kansu, a wannan alhamis sun fara taro don tattauna batutuwan da suka shafi kare muhalli a birnin Nairobi na Kenya da ake kira One Planet Summit.
Wallafawa ranar:
Wakilai sama da dubu hudu daga sassan duniya ne ke halartar taron, wanda ke cikin jerin tarurukan da Faransa ta bukaci a yi domin samar da kudaden da za a magance matsalar dumamar yanayi, bayan kulla yarjejeniyar duniya kan wannan batu a 2017 a birnin Paris.
Duk da cewa rawar da Afirka ke takawa wajen gurbata muhalli a duniya ba ta wuce 4% ba, to amma 65% na al’ummar nahiyar ne matsalar dumamar yanayin ta shafa, abin da masana ke cewa ya zama wajibi a dauki matakin taimaka wa nahiyar ta Afirka.
Shugaban Kenya Uhuru Kenyatta da takwaransa na Faransa Emmanuel Macron za su gabatar da jawabai ga taron a wannan alhamis.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu