Isa ga babban shafi
Rasha-Taliban

Rasha za ta shiga tsakani a rikicin Taliban da Afghanistan

Rasha za ta zamo mai shiga tsakani a tattaunawar zaman lafiya game da rikicin Afghanistan inda za ta karbi wakilcin bangarorin biyu a ranar 9 ga watan nan na Nuwamba wanda ake fatan ya kawo karshen rikicin kasar da aka shafe shekaru ana tafkawa.

Wannan ne dai karon farko da Taliban ke amincewa da makamanciyar tattaunawar wadda ake fatan ta kawo karshen rikicin da aka shafe shekaru ana yi a kasar.
Wannan ne dai karon farko da Taliban ke amincewa da makamanciyar tattaunawar wadda ake fatan ta kawo karshen rikicin da aka shafe shekaru ana yi a kasar. REUTERS/Stringer
Talla

A cewar Rasha ilahirin bangarorin kungiyar ta Taliban da bangaren gwamnati karkashin shugaba Ashraf Ghani sun amince da tura wakilai don tattaunawar wadda ita ce irinta ta farko da Taliban da amince da gudanarwa.

Sai dai ministan harkokin wajen Afghanistan Sebhgatullah Ahmadi ya ce kawo yanzu bazu kammala cimma yarjejeniya game da tattaunawar ba.

A bangare guda wannan ne karon farko da Taliban ta amince da tattaunawar kawo karshen rikicin na su da aka shafe shekaru ana fafatawa ko da dai ilahirin bangarorin biyu sun aminta da tsagaita wutar da suka yi watannin baya wanda a lokacin gwamnati ta bukaci dorewarta amma Taliban ta Bijire.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.