Rasha ta yi luguden wuta ta sama a yankin Idlib na Syria
Jiragen yakin Rasha sun kaddamar da wasu tagwayen hare-hare ta sama kan yankin Idlib na Syria, Yanki daya kuma mafi girma da ya rage a hannun ‘yan tawayen kasar.
Wallafawa ranar:
Sabbin hare haren na zuwa ne kwana daya bayan Turkiyya mai goyon bayan ‘yan tawaye, da Rasha da Iran masu marawa gwamnatin Syria baya sun gaza cimma matsaya a Tehran kan hanyar da za a bi wajen kauce wa sabon rikicin a yankin na Idlib da ke yankin arewa maso yammacin Syria.
Jaridar Monitor ta ruwaito cewa, cikin kasa da sa’a 3 jirage kusan 60 ne suka yi luguden wuta a yankin da ke gab da kan iyakar Syria da Turkiyya, duk kuwa da bukatar dakatar da hare-haren da Majalisar Dinkin Duniya ta yi.
Kusan wata guda kenan jiragen Yakin na Rasha na kokarin kai farmaki yankin na Idlib don fatattakar sauran ‘yan tawayen da suka rage.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu