Isa ga babban shafi
Kamaru-China

Shugaban Kamaru Paul Biya na ziyarar aiki kasar China

Shugaban Kamaru Paul Biya na ziyarar aiki a kasar China da zummar janyo hankulan masu zuba jari zuwa kasar sa.

Paul Biya, shugaban kasar Kamaru.
Paul Biya, shugaban kasar Kamaru. REUTERS/Philippe Wojazer
Talla

Fadar shugaban Kamaru ta ce ziyarar za ta taimaka wajen bunkasa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu.

Ma’aikatar tattalin arzikin Kamaru ta ce tun ranar lahadi shugaba Biya ya isa Beijing amma kuma a yau alhamis ne zai fara gana da mahukuntan China da kuma ‘Yan kasuwa.

Kawo yanzu dai China ce babbar abokiyar cinikin Kamaru, inda alkalumma ke nuni da cewa a shekarar 2015 an samu cinikin da ya kai sama da Dala biliyan biyu da rabi tsakanin kasashen biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.