Kwamitin Tsaro ya gaza samar da tsagaita wuta a Syria
Rasha ta shaida wa taron Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, babu wata yarjejeniyar tsagaita musayar wuta ta kwanaki 30 a Syria, yayin da ta bukaci a aiwatar da gyara ga daftarin kudirin tsarin shigar da kayayyakin agaji da kwashe fararen hula a yankin Ghouta mai fama da hare-haren dakarun gwamnati.
Wallafawa ranar:
Kusan makwanni biyu kenan da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ke kokarin cimma matsaya kan kudirin tsagaita wuta a daidai lokacin da dakarun gwamnatin kasar ke ci gaba da ragargazar yankin Ghouta da ke hannun ‘yan tawaye.
Jakadan Rasha a Majalisar, Vassily Nebenzia ya ce, kasashen Sweden da Kuwait da suka bukaci kada kuri’a a kan kudirin, na da cikakkiyar masaniyar cewa, babu wata yarjejeniya a kasa game da haka.
Nebenzia ya ce, Kwamitin Sulhun na bukatar cimma yarjejeniya mai yiwuwa amma ba wadda za ta kasance mai tsauri har ma a gaza aiwatar da ita.
Tuni kasashen Amurka, Faransa da Birtaniya suka bukaci Kwamitin da ya gaggauta kada kuri’a kan batun.
Sama da mutane 400 ne suka rasa rayukansu a cikin kwanaki biyar sakamakon farmakin sojin gwamnatin Syria a yankin gabashin Ghouta, lamarin da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana tamkar wutar jahannama a doran kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu