Zanga-zanga ta mamaye taron G20 a Hamburg
Shugabannin kasashe 20 masu karfin tattalin arzikin duniya G20 sun shiga rana ta karshe a taron da suke gudanarwa a Hamburg na Jamus da ke fuskantar zanga-zangar dubban mutane.
Wallafawa ranar:
Batutuwan da ake sa ran za su mamaye taron a yau rana ta karshe sun hada da fahimtar manufofin Donald Trump na Amurka musamman batun cinikayya da kuma canjin yanayi bayan ya yi watsi da yarjejeniyar Paris.
Zanga-zangar adawa da taron na G20 na ci gaba da kazancewa a Hamburg inda aka rahotanni suka ce ‘yan sanda su yi harbi sama domin tarwatsa masu zanga-zangar.
‘Yan sanda sun nemi karin jami’an tsaro a Hamburg sakamakon arangamarar da suke yi da masu zanga-zangar.
Rahotanni sun ce matar Donald Trump na amurka ta yi lattin isa taron matan shugabannin kasashen na G20 da wuri bayan masu zanga-zangar sun hana ta fita a gidan da ta sauka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu