Za'a Sake Zaman Tattauna Rikicin Syria a Geneva Ranar 10 ga Watan Gobe
Tattaunawar sulhu gameda yakin da ake yi a kasar Syria, wanda Majalisar Dinkin Duniya ke daukan nauyin shiryawa zai gudana ne ranar 10 ga watan gobe a Geneva.
Wallafawa ranar:
Jakadan Majalisar Staffan de Mistura ya sanar da haka yau inda yake cewa za’a ci gaba da tattaunawan ne a cikin watan Augusta da Satumba na wannan shekara.
Ranar 19 ga watan jiya aka yi tattaunawan sulhu na karshe.
Su dai ‘yan adawa a Syria sun tsaya kai da fata sai Shugaba Bashar Assad ya sauka kafin dukkan sulhu.
Mutane akalla dubu 320 suka mutu sakamakon wannan yaki da ake yi a Syria tun shekara ta 2011.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu