Isa ga babban shafi
Syria

Za'a Sake Zaman Tattauna Rikicin Syria a Geneva Ranar 10 ga Watan Gobe

Tattaunawar sulhu gameda yakin da ake yi a kasar Syria, wanda Majalisar Dinkin Duniya ke daukan nauyin  shiryawa  zai gudana ne ranar 10 ga watan gobe a Geneva.

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya Staffan de Mistura
Jakadan Majalisar Dinkin Duniya Staffan de Mistura REUTERS/Pierre Albouy/File Photo
Talla

Jakadan Majalisar Staffan de Mistura ya sanar da haka yau inda yake cewa za’a ci gaba da tattaunawan ne a cikin watan Augusta da Satumba na wannan shekara.

Ranar 19 ga watan jiya aka yi tattaunawan sulhu na karshe.

Su dai ‘yan adawa a Syria sun tsaya kai da fata  sai Shugaba Bashar Assad ya sauka kafin dukkan sulhu.

Mutane akalla dubu 320 suka mutu sakamakon wannan yaki da ake yi a Syria tun shekara ta 2011.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.