Jamus ta dauki alhakin kisan Yahudawa
Kasar Jamus ta ce ta dauki alhakin kisan gillar da Adolf Hitler ya yiwa Yahudawa bayan Firaminstan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa shugaban Falasdinawa ne ya bai wa Hitler shawarar hallaka su.
Wallafawa ranar:
Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce ba su ga dalilin jawabin na Netanyahu ba, wadda ta ce na neman sauya tarihin da aka sani ne.
A ziyarar da ya ke yi a Jamus, Netanyahu ya bayyana cewa Hitler bai da shirin kashe Yahudawa har sai da ya hadu da shugaban Falasdinawa Haj Amin Al Hussein, babban limamin birnin Qudus wanda ya ba shi shawarar hallaka su saboda kar ya ba su damar koma wa birnin Qudus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu